3. Sai ya yi annabcinsa, ya ce.“Faɗar Bal'amu ɗan Beyor,Faɗar mutumin da idonsa take a buɗe.
4. Faɗar wanda yake jin faɗar Allah,Shi wanda yake ganin wahayin Maɗaukaki,Yana durƙushe, amma idanunsa a buɗe suke.
5. Alfarwan Isra'ilawa suna da kyan gani!
6. Kamar dogon jerin itatuwan dabino,Kamar gonaki a gefen kogi,Kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa,Kamar kuma itatuwan al'ul a gefen ruwaye.
7. Sojojin Isra'ilawa za su sa al'ummai rawar jiki;Za su yi mulkin jama'a mai yawaSarkinsu zai fi Agag girma,Za a ɗaukaka mulkinsa.