15. Shugaban rundunar kabilar mutanen Issaka Netanel ne, ɗan Zuwar.
16. Shugaban rundunar kabilar mutanen Zabaluna Eliyab ne, ɗan Helon.
17. Sa'an nan aka kwankwance alfarwar, sai 'ya'yan Gershon, da 'ya'yan Merari masu ɗaukar alfarwar suka kama hanya.
18. Tutar zangon kabilar mutanen Ra'ubainu ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Elizur ne, ɗan Shedeyur.
19. Shugaban rundunar kabilar mutanen Saminu kuwa Shelumiyel ne, ɗan Zurishaddai.
20. Shugaban rundunar kabilar mutanen Gad Eliyasaf ne, ɗan Deyuwel.
21. Daga nan sai Kohatawa masu ɗauke da kayayyaki masu tsarki suka tashi. Kafin su isa masaukin, an riga an kafa alfarwar.
22. Tutar zangon mutanen Ifraimu ta tashi, ƙungiyoyinsu na biye. Shugaban rundunarsu Elishama ne, ɗan Ammihud.
23. Shugaban rundunar kabilar mutanen Manassa Gamaliyel ne, ɗan Fedazur.
24. Shugaban rundunar kabilar mutanen Biliyaminu Abidan ne, ɗan Gideyoni.
25. A ƙarshe sai ƙungiyar mutanen Dan da take bayan dukan zangon, ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Ahiyezer ne, ɗan Ammishaddai.
26. Shugaban rundunar kabilar mutanen Ashiru Fagiyel ne, ɗan Okran.
27. Shugaban rundunar kabilar mutanen Naftali Ahira ne, ɗan Enan.
28. Wannan shi ne tsarin tafiyar Isra'ilawa bisa ga rundunansu sa'ad da sukan tashi.
29. Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamadayane, surukinsa, “Muna kan hanya zuwa wurin da Ubangiji ya ce zai ba mu, ka zo tare da mu, za mu yi maka alheri, gama Ubangiji ya alkawarta zai yi wa Isra'ila alheri.”
30. Amma ya ce masa, “Ba zan tafi ba, zan koma ƙasata da wurin dangina.”
31. Musa kuwa ya ce masa, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu, gama ka san jejin da muke zango, kai za ka zama idonmu.
32. Idan ka tafi tare da mu, kowane irin alheri da Ubangiji zai yi mana, mu kuma haka za mu yi maka.”
33. Sai suka tashi daga dutsen Ubangiji, wato Sinai, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji kuwa ya wuce gabansu don ya nemar musu masauki.
34. A duk lokacin da suka tashi daga zango, sai girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35. Duk kuma lokacin da akwatin zai tashi, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji, ka sa maƙiyanka su warwatse, ka sa waɗanda suke ƙinka su gudu gabanka.”