Ish 49:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ku kasa kunne gare ni, ku al'ummai manisanta,Ku mutanen da suke zaune a can nesa!Ubangiji ya zaɓe ni, tun kafin a haife ni,Ya kuwa sa ni in zama bawansa.

2. Ya sa maganata ta yi kaifi kamar takobi,Ya kiyaye ni da ikonsa.Ya sa na zama kamar kibiyaMai tsini shirayayyiya domin harbi.

3. Ya ce mini, “Isra'ila, kai bawana ne.Mutane za su yabe ni saboda kai.”

4. Na ce, “Na yi aiki, amma a banza ne.Na mori ƙarfina, amma ban ƙulla kome ba.”Duk da haka na dogara ga Ubangiji, ya daidaita al'amura,Shi zai sāka mini abin da na yi.

Ish 49