1. Ku kasa kunne gare ni, ku al'ummai manisanta,Ku mutanen da suke zaune a can nesa!Ubangiji ya zaɓe ni, tun kafin a haife ni,Ya kuwa sa ni in zama bawansa.
2. Ya sa maganata ta yi kaifi kamar takobi,Ya kiyaye ni da ikonsa.Ya sa na zama kamar kibiyaMai tsini shirayayyiya domin harbi.