1. Sairus shi ne zaɓaɓɓen sarki na Ubangiji!Ubangiji ya sa shi ya ci al'ummai,Ya aike shi ya tuɓe ikon sarakuna,Ubangiji zai buɗe masa ƙofofin birni.Ubangiji ya ce wa Sairus,
2. “Ni kaina zan shirya hanya dominka,Ina baji duwatsu da tuddai.Zan kakkarye ƙyamaren tagulla,In kuma daddatse gagara badau na baƙin ƙarfe.