Ish 2:8-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ƙasarsu tana cike da gumaka, suna sujada ga abubuwan da suka yi da hannuwansu.

9. Za a ƙasƙantar da kowane mutum, a kunyata shi. Kada ka gafarta musu, ya Ubangiji!

10. Za su ɓuya a cikin kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa!

Ish 2