1. Sa'ad da Ezra yake yin addu'a, yana hurta laifi, yana kuka, yana a durƙushe gaban Haikalin Allah, sai babban taron jama'a, mata, da maza, da yara daga Isra'ila suka taru wurinsa. Mutane suka yi kuka mai zafi.
2. Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam, ya yi wa Ezra magana, ya ce, “Mun yi wa Allahnmu rashin aminci, gama mun auri mata baƙi daga mutanen ƙasar, amma duk da haka akwai sauran bege ga Isra'ila.
3. Bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori dukan waɗannan mata da 'ya'yansu, bisa ga shawarar shugabanni da waɗanda suke rawar jiki saboda umarnin Allah. Bari mu yi alkawari bisa ga doka.
4. Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, mu kuwa muna tare da kai. Sai dai ka yi ƙarfin hali, ka yi shi.”
5. Ezra kuwa ya tashi, ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra'ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
20-24. Na iyalin Immer, Hanani, da ZabadiyaNa iyalin Harim, Ma'aseya, da Iliya, da Shemaiya, da Yehiyel, da UzziyaNa iyalin Fashur, Eliyehoyenai, da Ma'aseya, da Isma'ilu, da Netanel, da Yozabad, da ElasaNa Lawiyawa, Yozabad, da Shimai, da Kelaya, wato Kelita, da Fetahiya, da Yahuza, da EliyezerNa mawaƙa, EliyashibNa masu tsaron ƙofa, Shallum, da Telem, da Uri
25-33. Akwai kuma waɗansu na Isra'ila.Na iyalin Farosh, Ramiya, da Izziya, da Malkiya, da Miyamin, da Ele'azara, da Malkiya, da BenaiyaNa iyalin Elam, Mattaniya, da Zakariya, da Yehiyel, da Abdi, da Yeremot, da IliyaNa iyalin Zattu, Eliyehoyenai, da Eliyashib, da Mattaniya, da Yeremot, da Zabad, da AzizaNa iyalin Bebai, Yehohanan,da Hananiya, da Zabbai, da AtlaiNa iyalin Bani, Meshullam, da Malluki, da Adaya, da Yashub, da Sheyal, da YeremotNa iyalin Fahat-mowab, Adana, da Kelal, da Benaiya, da Ma'aseya, da Mattaniya, da Bezalel, da Binnuyi, da ManassaNa iyalin Harim, Eliyezer, da Isshiya, da Malkiya, da Shemaiya, da Shimeyon, da Biliyaminu, da Malluki, da ShemariyaNa iyalin Hashum, Mattenai, da Mattatta, da Zabad, da Elifelet, da Yeremai, da Manassa, da Shimai
34-37. Na iyalin Bani, Mayadi, da Amram, da Yuwel, da Benaiya, da Bedeya, da Keluhi, da Waniya, da Meremot, da Eliyashib, da Mattaniya, da Mattenai, da Yawasu
38-42. Na iyalin Binnuyi, Shimai, da Shelemiya, da Natan, da Adaya, da Maknadebai, da Shashai, Sharai, da Azarel, da Shelemiya, da Shemariya, da Shallum, da Amariya, da Yusufu