2 Sam 22:48-51 Littafi Mai Tsarki (HAU)

48. Ya ba ni nasara a kan abokan gabana,Ya sa mutane a ƙarƙashin mulkina,

49. Ya kuɓutar da ni daga hannun maƙiya.Kai, ya Ubangiji, ka ba ni nasara a kan maƙiyana,Ka tsare ni daga mutane masu zafin hali.

50. Domin wannan zan yi yabonka cikin al'ummai,Zan raira yabbai gare ka.

51. Allah ya ba sarkinsa manya manyan nasarori,Ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shi wanda ya zaɓa,Wato ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

2 Sam 22