1 Tar 16:7-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. A wannan lokaci ne Dawuda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su riƙa raira waƙoƙin yabo ga Ubangiji.

8. Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa,Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!

9. Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi,Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi!

10. Ku yi murna saboda mu nasa ne,Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!

11. Ku je wurin Ubangiji neman taimako,Ku tsaya a gabansa koyaushe.

12. Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki,Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.

13. Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim,Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu.

14. Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu,Umarnansa domin dukan duniya ne.

1 Tar 16