13. Sa'an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefe, ya tsaya can nesa bisa dutsen, da ɗan nisa tsakaninsu.
14. Sai Dawuda ya kira sojojin sansanin, da kuma Abner ɗan Ner, ya ce, “Ba za ka amsa mini ba, Abner?”Sai Abner ya ce, “Wa yake kiran sarki?”
15. Dawuda ya ce wa Abner, “Kai ba namiji bane? Wa yake kama da kai cikin Isra'ila? Me ya sa ba ka lura da mai girma, sarki ba? Wani mutum ya zo don ya hallaka mai girma sarki.
16. Abin da ka yi ba shi da kyau. Ka isa a kashe ka, da yake ba ka lura da mai girma ba, wanda Ubangiji ya keɓe. Ka duba, ina mashin sarki da butar ruwan da yake wajen kansa suke?”