6. Su yi girma har su yi huda,Sa'an nan su yi yaushi su bushe da yamma.
7. Mun halaka ta wurin fushinka,Mun razana saboda hasalarka.
8. Ka jera zunubanmu a gabanka,Zunubanmu na ɓoye kuwa,Ka sa su a inda za ka gan su.
9. Fushinka ya gajerta tsawon ranmu,Ranmu ya ƙare kamar ajiyar zuciya.
10. Tsawon kwanakin ranmu duka a ƙalla shekara ce saba'in,In kuwa muna da ƙarfi, shekara tamanin ne.Duk da haka iyakar abin da waɗannan shekaruSuke kawo mana, damuwa ce da wahala,Nan da nan sukan wuce,Tamu da ƙare.