Zab 78:5-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Ya ba da dokoki ga jama'ar Isra'ila,Da umarnai ga zuriyar Yakubu.Ya ba kakanninmu ka'idodi,Don su koya wa 'ya'yansu dokokinsa,

6. Saboda tsara mai zuwa ta koye su,Su kuma su koya wa 'ya'yansu.

7. Ta haka su ma za su dogara ga Allah,Ba za su manta da abin da ya yi ba,Amma a kullum za su riƙa biyayya da umarnansa.

Zab 78