Zab 71:4-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Ya Allahna, ka cece ni daga mugaye,Daga ikon mugga, wato mugayen mutane.

5. Ya Ubangiji, a gare ka nake sa zuciya,Tun ina yaro, nake dogara gare ka.

6. A duk kwanakina a gare ka nake dogara,Kana kiyaye ni tun da aka haife ni,Kullayaumi zan yabe ka!

7. Raina abin damuwa ne ga mutane da yawa,Amma kai ne kāriyata mai ƙarfi.

8. Ina yabonka dukan yini,Ina shelar darajarka.

Zab 71