1. Da ma Allah ya tashi ya warwatsa maƙiyansa!Da ma su waɗanda suke ƙinsa su gudu!
2. Kamar yadda iska take korar hayaƙi,Haka nan zai kore su,Kamar yadda kākin zuma yakan narke a gaban wuta,Haka nan mugaye za su hallaka a gaban Allah.
3. Amma adalai za su yi murna,Su kuma yi farin ciki a gaban Allah,Za su yi murna ƙwarai da gaske.