Zab 68:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Da ma Allah ya tashi ya warwatsa maƙiyansa!Da ma su waɗanda suke ƙinsa su gudu!

2. Kamar yadda iska take korar hayaƙi,Haka nan zai kore su,Kamar yadda kākin zuma yakan narke a gaban wuta,Haka nan mugaye za su hallaka a gaban Allah.

3. Amma adalai za su yi murna,Su kuma yi farin ciki a gaban Allah,Za su yi murna ƙwarai da gaske.

Zab 68