7. Amma Allah zai harbe su da kibansa,Za a yi musu rauni nan da nan.
8. Zai hallaka su saboda maganganunsu,Duk wanda ya gan su zai kaɗa kansa.
9. Dukansu za su ji tsoro,Za su faɗi abin da Allah ya aikata,Su yi tunani a kan ayyukansa.
10. Dukan masu adalci za su yi murna,Saboda abin da Ubangiji ya aikata.Za su sami mafaka a gare shi,Dukan mutanen kirki za su yabe shi.