3. Ka aiko da haskenka, da gaskiyarka,Bari su bishe ni,Su kawo ni Sihiyona, tsattsarkan tudunka,Su kawo ni Haikalinka, inda zatinka yake!
4. Sa'an nan zan tafi wurin bagadenka, ya Allah,Zuwa gare ka, kai wanda kake sa ni in yi murna da farin ciki,In raira waƙar yabo a gare ka da garayata,Ya Allah, Allahna!
5. Me ya sa nake baƙin ciki?Me ya sa nake damuwa?Zan dogara ga Allah,Zan ƙara yabonsa,Mai Cetona, Allahna.