29. Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar,Su gāje ta har abada.
30. Kalmomin mutumin kirki suna da hikima,Yana faɗar abin da yake daidai.
31. Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau.
32. Mugu yakan yi fakon mutumin kirki,Yă yi ƙoƙari yă kashe shi,
33. Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba,Ko kuwa yă bari a kāshe shiSa'ad da ake masa shari'a.