Zab 37:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Gama Ubangiji zai raba mugaye da ƙarfinsu,Amma zai kiyaye mutanen kirki.

18. Ubangiji yana kula da masu yi masa biyayya,Ƙasar kuwa za ta zama tasu har abada.

19. Ba za su sha wahala a lokacin tsanani ba,Za su sami yalwa a lokacin yunwa.

20. Amma mugaye za su mutu,Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji,Za su ɓace kamar hayaƙi.

21. Mugu yakan ci bashi, yă ƙi biya,Amma mutumin kirki mai alheri ne,Mai bayarwa hannu sake.

Zab 37