Zab 25:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A gare ka nake yin addu'a, ya Ubangiji,

2. A gare ka nake dogara, ya Allah.Ka cece ni daga shan kunyar fāɗuwa,Kada ka bar magabtana su yi mini duban wulakanci!

3. Waɗanda suke dogara gare ka,Ba za su kasa yin nasara ba,Sai dai waɗanda suke gaggawa su yi maka tayarwa.

4. Ka koya mini al'amuranka, ya Ubangiji,Ka sa su zama sanannu a gare ni.

Zab 25