Zab 2:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ka yi roƙo, zan kuwa ba ka dukan al'ummai,Dukan duniya kuma za ta zama taka.

9. Za ka mallake su da sandan ƙarfe,Za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu.’ ”

10. Yanzu ku kasa kunne gare ni, ku sarakuna,Ku mai da hankali, ku mahukunta!

11. Ku bauta wa Ubangiji da tsoro,Ku yi rawar jiki, ku rusuna masa,

Zab 2