5. Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka,Saninsa ya fi gaban aunawa.
6. Yakan ɗaukaka masu tawali'u,Amma yakan ragargaza mugaye har ƙasa.
7. Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,Ku yabi Allah da garaya.
8. Ya shimfiɗa gajimare a sararin al'arshi.Ya tanada wa duniya ruwan sama,Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai.