Zab 138:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Da zuciya ɗaya nake gode maka, ya Ubangiji,Ina raira waƙar yabonka a gaban alloli.

2. Na durƙusa a gaban tsattsarkan HaikalinkaIna yabon sunanka.Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka,Saboda ka nuna ɗaukakarka da umarnanka.

3. Ka amsa mini sa'ad da na yi kira gare ka,Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni.

Zab 138