1. Da zuciya ɗaya nake gode maka, ya Ubangiji,Ina raira waƙar yabonka a gaban alloli.
2. Na durƙusa a gaban tsattsarkan HaikalinkaIna yabon sunanka.Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka,Saboda ka nuna ɗaukakarka da umarnanka.
3. Ka amsa mini sa'ad da na yi kira gare ka,Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni.