Zab 122:5-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. A nan majalisu suke,Wurin da sarki yake yi wa jama'arsa shari'a.

6. Ku yi wa Urushalima addu'ar salama!“Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta!

7. Salama ta samu a garukanki,Da zaman lafiya kuma a fādodinki.”

8. Saboda abokaina da aminaina,Na ce wa Urushalima, “Salama a gare ki!”

9. Saboda Haikalin Ubangiji, Allahnmu,Ina addu'a domin ki arzuta.

Zab 122