1. Ka cece ni, ya Ubangiji,Ba sauran mutanen kirki,Ba kuma za a sami amintattun mutane ba.
2. Dukan mutane suna yi wa juna ƙarya,Suna ruɗin junansu da yaudara.
3. Ka sa harsunan nan masu yaudara su yi shiru,Ya Ubangiji, ka rufe bakunan nan masu fāriya!
4. Sukan ce, “Za mu yi magana yadda muka ga dama,Ba kuwa wanda zai hana mu.Wane ne yake da ikon faɗa mana abin da za mu faɗa?”