Zab 116:16-18-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Ni bawanka ne, ya Ubangiji,Ina bauta maka yadda mahaifiyata ta yi,Ka 'yantar da ni.

17. Zan miƙa maka hadaya ta godiya,Zan yi addu'ata a gare ka.

18-19. A taron dukan jama'arka,A shirayun Haikalinka,A Urushalima, zan ba ka abin da na alkawarta.Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zab 116