41. Ya tsamo masu bukata daga cikin baƙin cikinsu,Ya sa iyalansu su riɓaɓɓanya kamar garkunan tumaki.
42. Da adalai suka ga wannan, sai suka yi murna,Mugaye kuwa aka rufe bakinsu.
43. Da ma a ce masu hikimaZa su yi tunani a kan waɗannan abubuwa,Da ma kuma su yardaDa madawwamiyar ƙaunar Ubangiji.