27. Zai warwatsa zuriyarsu a cikin arna,Ya bar su su mutu a baƙuwar ƙasa.
28. Sai jama'ar Allah suka taru suka shiga yi wa Ba'al sujada, a Feyor,Suka ci hadayun da aka miƙa wa matattun alloli.
29. Suka tsokani Ubangiji, ya yi fushi saboda ayyukansu,Mugawar cuta ta auka musu,
30. Amma Finehas ya tashi, ya yanke hukunci a kan laifin,Aka kuwa kawar da annobar.