Zab 106:27-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Zai warwatsa zuriyarsu a cikin arna,Ya bar su su mutu a baƙuwar ƙasa.

28. Sai jama'ar Allah suka taru suka shiga yi wa Ba'al sujada, a Feyor,Suka ci hadayun da aka miƙa wa matattun alloli.

29. Suka tsokani Ubangiji, ya yi fushi saboda ayyukansu,Mugawar cuta ta auka musu,

30. Amma Finehas ya tashi, ya yanke hukunci a kan laifin,Aka kuwa kawar da annobar.

Zab 106