Zab 105:8-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Zai cika alkawarinsa har abada,Alkawaransa kuma don dubban zamanai,

9. Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim,Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.

10. Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila,Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce,

11. “Zan ba ka ƙasar Kan'ana,Za ta zama mallakarka.”

12. Jama'ar Ubangiji kima ne,Baƙi ne kuwa a ƙasar.

13. Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa,Daga wannan mulki zuwa wancan,

14. Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba,Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su.

15. Ya ce, “Kada ku taɓi bayina, zaɓaɓɓu,Kada ku cuci annabawana!”

16. Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu,Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare,

Zab 105