4. Ku je wurin Ubangiji neman taimako,Ku tsaya a gabansa koyaushe.
5-6. Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim,Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu,Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki,Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.
7. Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu,Umarnansa domin dukan duniya ne.