28. Ka ba su, sun ci,Ka tanada musu abinci, sun ƙoshi.
29. Sa'ad da ka rabu da su sukan tsorata,In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu,Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su.
30. Amma sa'ad da ka hura musu numfashi, sai su rayu,Kakan sabunta fuskar duniya.