19. Zan ɗaura auren da yake cikin adalci,Da bisa kan ka'ida, da ƙauna.
20. Zan ɗaura auren da yake cikin aminci,Za ki kuwa sani, ni ne Ubangiji.
21. “A waccan rana, zan amsa wa sammai,Su kuma za su amsa wa ƙasa.
22. Ƙasa kuma za ta amsa wa hatsi, da ruwan inabi, da mai,Su ma za su amsa wa Yezreyel.
23. Zan dasa ta a ƙasa domin kaina.Zan kuma yi wa ‘Ba-jinƙai,’ jinƙai,In kuma ce wa ‘Ba-mutanena ba,’ ‘Mutanena!’Su ma za su ce, ‘Kai ne Allahna!’ ”