28. “Bayan wannan zan zubo Ruhuna akan jama'a duka,'Ya'yanku mata da maza za su iyarda saƙona,Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai,Samarinku za su ga wahayi da yawa.
29. A lokacin zan zubo Ruhuna,Har a kan barori mata da maza.
30. “Zan yi faɗakarwa a kan wannanranaA sararin sama da a duniya.Za a ga jini, da wuta, da murtukewarhayaƙi,
31. Rana za ta duhunta,Wata zai zama ja wur kamar jini,Kafin isowar babbar ranan nan maibantsoro ta Ubangiji.