26. Sai suka ce masa, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe maka ido?”
27. Ya amsa musu ya ce, “Na riga na faɗa muku, ba ku ji ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?”
28. Sai suka fāɗa shi da zagi, suna cewa, “Kai ne dai almajirin wannan ɗin, mu kam, almajiran Musa ne.
29. Mun dai sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan ba mu san ta inda ya fito ba.”