13. Amma ba wanda ya yi magana tasa a fili don tsoron Yahudawa.
14. Wajen tsakiyar idin sai Yesu ya shiga Haikali ya koyar.
15. Yahudawa suka yi mamakin abin, suka ce, “Yaya mutumin nan yake da karatu haka, ga shi kuwa, bai taɓa koyo ba?”
16. Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta wanda ya aiko ni ce.