Yah 6:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.

4. To, Idin Ƙetarewa, wato idin Yahudawa, ya gabato.

5. Da Yesu ya ɗaga kai ya hango babban taro yana doso shi, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayo gurasar da mutanen nan za su ci?”

6. Ya faɗi haka ne fa domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.

7. Filibus ya amsa ya ce, “Ai, ko gurasar dinari metan ma ba ta isa ko wannensu ya sami kaɗan ba.”

Yah 6