5. A nan kuwa akwai wani mutum da ya shekara talatin da takwas da rashin lafiya.
6. Da Yesu ya gan shi kwance, ya kuma sani ya daɗe da wannan hali, sai ya ce masa, “Kana so a warkar da kai?”
7. Marar lafiyar ya amsa masa ya ce, “Ya Shugaba, ai, ba ni da wanda zai angaza ni cikin ruwan lokacin da aka motsa shi. Lokacin da na doshi ruwan kuma sai wani ya riga ni shiga.”
8. Sai Yesu ya ce masa, “Tashi, ka ɗauki shimfiɗarka, ka yi tafiya!”
9. Nan take mutumin ya warke, ya ɗauki shimfiɗarsa ya yi tafiya tasa.Ran nan kuwa Asabar ce.