Yah 4:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. sai ya bar ƙasar Yahudiya, ya koma ƙasar Galili.

4. Lalle ne kuwa yă ratsa ƙasar Samariya.

5. Sai ya zo wani gari na ƙasar Samariya, wanda ake kira Saikar, kusa da yankin ƙasar da Yakubu ya ba ɗansa Yusufu.

6. Rijiyar Yakubu kuwa a nan take. Saboda gajiyar tafiya fa, sai Yesu ya zauna haka nan a bakin rijiyar. Wajen tsakar rana ce kuwa.

7. Sai ga wata Basamariya ta zo ɗiban ruwa. Yesu ya ce mata, “Sa mini ruwa in sha.”

Yah 4