Yah 21:9-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Da fitowarsu gaci sai suka ga garwashi a wurin, da kifi kai, da kuma gurasa.

10. Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifi a na waɗanda kuka kama yanzu.”

11. Sai Bitrus ya hau jirgin, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu haka, tarun bai kece ba.

12. Sai Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Daga cikin almajiran kuwa ba wanda ya yi ƙarfin halin tambayarsa ko shi wane ne, domin sun sani Ubangiji ne.

Yah 21