4. Yesu kuwa da ya san duk abin da zai same shi, ya yiwo gaba, ya ce musu, “Wa kuke nema?”
5. Suka amsa masa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce musu, “Ni ne.” Yahuza kuwa da ya bāshe shi yana tsaye tare da su.
6. Da Yesu ya ce musu, “Ni ne,” suka ja da baya da baya, har suka fāɗi.
7. Sai ya sāke tambayarsu, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.”
8. Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku, ni ne. In kuwa ni kuke nema, ku bar waɗannan su tafi.”
9. Wannan kuwa domin a cika maganar da ya yi ne cewa, “A cikin waɗanda ka ba ni ban yar da ko ɗaya ba.”
10. Bitrus kuwa da yake yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama. Sunan bawan Malkus.