16. Lokacin da ta zo wurin surukarta, sai surukarta ta ce mata, “'Yata, ina labari?”Sai ta faɗa mata dukan abin da mutumin ya faɗa mata.
17. Ta kuma ce, “Ga sha'ir da ya ba ni, gama ya ce, ‘Ba za ki koma wurin surukarki hannu wofi ba.’ ”
18. Sai surukarta ta ce, “Ki jira dai, 'yata, har ki ga yadda al'amarin zai zama, gama mutumin ba zai huta ba, sai ya daidaita al'amarin a yau.”