Rom 9:30-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. To, me kuma za mu ce? Ga shi, al'ummai da ba su nace da neman adalcin Allah ba, sun samu, wato, sun sami adalcin da yake daga bangaskiya.

31. Isra'ila kuwa da suka nace da neman hanyar adalcin Allah, suka kasa samunta.

32. Me ya sa? Don ba su neme ta ta hanyar bangaskiya ba, sai dai ta hanyar aikata aikin lada. Sai suka yi tuntuɓe da dutsen tuntuɓe,

33. kamar yadda yake a rubuce cewa,“Ga shi, na sa dutsen sa tuntuɓe a Sihiyona,Da fā na sa faɗuwa.Duk mai gaskatawa da shi, ba zai kunyata ba.”

Rom 9