Rom 9:21-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Ashe, maginin tukwane ba ya iko da yumɓu, ya gina wata domin aiki mai martaba, wata kuma don kasasshen aiki, duk daga curi ɗaya?

22. To, ƙaƙa fa? Allah da yake yana so ya nuna fushinsa, ya kuma bayyana ikonsa, sai ya haƙura matuƙar haƙuri da waɗanda suka cancanci fushinsa, suka kuma isa hallaka,

23. Nufinsa ne yă bayyana yalwar ɗaukakarsa ga waɗanda ya yi wa jinƙai, wato, waɗanda dā ma ya yi wa tanadin ɗaukaka?

24. Wato, mu ke nan da ya kira, ba kuwa daga cikin Yahudawa kaɗai ba, har ma daga cikin al'ummai.

25. Kamar dai yadda ya faɗa a Littafin Yusha'u cewa,“Waɗanda dā ba jama'ata ba,Zan ce da su ‘jama'ata,’Wadda dā ba abar ƙaunata ba kuma,Zan ce da ita ‘abar ƙaunata.’ ”

26. “A daidai wurin da aka ce da su, ‘Ku ba jama'ata ba ne,’A nan ne za a kira su ‘'ya'yan Allah Rayayye,’ ”

Rom 9