4. Birnin yana da faɗi da girma, amma mutanen da suke ciki kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje ba tukuna.
5. Allahna kuwa ya sa a zuciyata in tara manya da shugabanni, da sauran jama'a don a rubuta su bisa ga asalinsu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara komowa. Ga abin da na tarar aka rubuta ciki.
6. Waɗannan su ne mutanen lardin Yahuza, waɗanda suka komo daga zaman talala da Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kai mutane. Sun komo Urushalima da Yahuza. Kowa ya tafi garinsu.
7. Sun komo tare da Zarubabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Seraiya, da Re'elaya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Rehum, da Ba'ana.
39-42. Ga lissafin iyalin firistoci da suka komo daga zaman talala.Yedaiya, na zuriyar Yeshuwa, ɗari tara da saba'in da ukuImmer, dubu ɗaya da hamsin da biyu (1,052)Fashur, dubu da ɗari biyu da arba'in da bakwai (1,247)Harim, dubu ɗaya da goma sha bakwai (1,017)
43. Lawiyawan da suka komo daga zaman talala, Yeshuwa da Kadmiyel na zuriyar Hodawiya, saba'in da huɗu.
44. Mawaƙa, na zuriyar Asaf, ɗari da arba'in da takwas.
45. Masu tsaron Haikali su ne zuriyar Shallum, da Ater, da Talmon, da Akkub, da Hatita, da Shobai, ɗari da talatin da takwas.
46-56. Ma'aikatan Haikali da suka komo daga zaman talala, su neZuriyar Ziha, da Hasufa, da Tabbawot,Keros, da Siyaha, da Fadon,Lebana, da Hagaba, da Shamlai,Hanan, da Giddel, da Gahar,Rewaiya, da Rezin, da Nekoda,Gazam, da Uzza, da Faseya,Besai, da Me'uniyawa, da Nefushiyawa,Bakbuk, da Hakufa, da Harkur,Bazlut, da Mehida, da Harsha,Barkos, da Sisera, da Tema,Neziya, da Hatifa.
57-59. Iyalan barorin Sulemanu da suka komo daga zaman talala, su nena Sotai, da Hassoferet, da Feruda,Yawala, da Darkon, da Giddel,Shefatiya, da Hattil, da Fokeret-hazzebayim, da Ami.
60. Jimillar zuriyar ma'aikatan Haikali da na Sulemanu, su ɗari uku da tasa'in da biyu ne.
61-62. Waɗannan su ne daga zuriyar Delaiya, da Tobiya, da Nekoda, waɗanda suka zo daga garuruwan Telmela, da Tel-harsha, da Kerub, da Addan, da Immer, amma ba su iya nuna gidajen kakanninsu, ko zuriyarsu a cikin Isra'ilawa ba, su ɗari shida ne da arba'in da biyu.
63. Na wajen firistoci kuma su ne zuriyar Habaya, da na Hakkoz, da na Barzillai, wanda ya auri 'yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kira shi da sunan zuriyar surukinsa.
64. Waɗannan suka nema a rubuta su tare da waɗanda aka rubuta jerin sunayen asalinsu, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
65. Sai mai mulki ya faɗa musu kada su ci abinci mafi tsarki, sai an sami firist wanda zai yi tambaya ta wurin Urim da Tummin tukuna.
66-69. Jimillar waɗanda suka komo duka su dubu arba'in da dubu biyu da ɗari uku da sittin ne (42,360)barorinsu mata da maza, waɗanda yawansu ya kai dubu bakwai da ɗari uku da talatin da bakwai (7,337)mawaƙa ɗari biyu da arba'in da biyar mata da mazadawakansu kuma ɗari bakwai da talatin da shida nealfadaransu kuma ɗari biyu da arba'in da biyar neraƙumansu ɗari huɗu da talatin da biyar nejakunansu dubu shida da ɗari bakwai da ashirin (6,720)
70-72. Da yawa daga cikin jama'a suka ba da taimako domin biyan aikin gyaran Haikali.Mai mulki ya ba dazinariya darik dubu (1,000)kwanonin wanke hannu guda hamsinrigunan firistoci ɗari biyar da talatinShugabannin iyali suka ba dazinariya darik dubu ashirin (20,000)azurfa maina dubu biyu da ɗari biyu (2,200)Sauran jama'a suka ba dazinariya darik dubu ashirin (20,000)azurfa maina dubu biyu (2,000)rigunan firistoci guda sittin da bakwai
73. Sa'an nan firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron Haikali, da mawaƙa da waɗansu da dama daga cikin jama'a, da ma'aikatan Haikali, da dukan Isra'ilawa suka zauna a garuruwansu.