Mika 1:4-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Duwatsu za su narke aƙarƙashinsa,Kwaruruka za su tsattsage kamarkakin zuma a gaban wuta,Kamar ruwa yana gangarowa dagatsauni.

5. Duk wannan kuwa saboda laifinYakubu ne,Da laifin Isra'ila.Mene ne laifin Yakubu?Ashe, ba bautar gumaka da zaluncinda ake yi a Samariya ba?Mene ne kuma laifin Yahuza?Ashe, ba bautar gumaka da zaluncinda ake yi a Urushalima ba?

6. “Domin haka zan mai da Samariyajujin kufai a karkara,Wurin dasa kurangar inabi.Zan zubar da duwatsunta a cikinkwari,In tone harsashin gininta.

7. Za a farfashe dukan siffofinta nazubi,Za a ƙaƙƙone dukiyarta da wuta,Zan lalatar da gumakanta duka,Gama ta wurin karuwanci ta samosu,Ga karuwanci kuma za su koma.”

Mika 1