19. Sai Yesu ya tashi, ya bi shi tare da almajiransa.
20. Ga kuma wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini, ta raɓo ta bayansa, ta taɓa gezar mayafinsa,
21. domin ta ce a ranta, “Ko da mayafinsa ma na taɓa, sai in warke.”
22. Sai Yesu ya juya, yă gan ta, ya ce, “'Yata, ki yi farin ciki, bangaskiyarki ta warkar da ke.” Nan take matar ta warke.
23. Da Yesu ya isa gidan shugaban jama'ar, ya kuma ga masu busar sarewa da taro suna ta hayaniya,