Mat 27:41-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

41. Haka kuma manyan firistoci da malaman Attaura da shugabanni suka riƙa yi masa ba'a, suna cewa,

42. “Ya ceci waɗansu, ya kuwa kasa ceton kansa. Ai, Sarkin Isra'ila ne, yă sauko mana daga gicciyen yanzu, mu kuwa mā gaskata da shi.

43. Yā dogara ga Allah, to, Allah ya cece shi mana yanzu, in dai yana sonsa, don ya ce wai shi Ɗan Allah ne.”

44. Har 'yan fashin nan da aka gicciye su tare ma, su suka zazzage shi kamar waɗancan.

45. To, tun daga tsakar rana, duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma.

Mat 27