Mat 26:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Da Yesu ya gama duk wannan magana, sai ya ce wa almajiransa,

2. “Kun san Idin Ƙetarewa saura kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum a gicciye shi.”

3. Sai manyan firistoci da shugabannin jama'a suka taru a gidan babban firist, mai suna Kayafa.

4. Suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci su kashe shi.

5. Amma suka ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kada jama'a su yi hargitsi.”

Mat 26