Mat 24:38-44 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. Kamar a kwanakin nan ne gabannin Ruwan Tsufana, ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har ya zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi,

39. ba su farga ba har Ruwan Tsufana ya zo ya share su. Haka komowar Ɗan Mutum za ta zama.

40. A sa'an nan za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.

41. Za a ga mata biyu suna niƙa, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.

42. To, ku zauna a faɗake fa, don ba ku san ranar da Ubangijinku zai dawo ba.

43. Amma dai ku sani, da maigida zai san ko a wane lokaci ne da dare ɓarawo zai zo, da ya zauna a faɗake ya hana a shigar masa gida.

44. Don haka ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba, Ɗan Mutum zai zo.”

Mat 24