Mat 22:35-41 Littafi Mai Tsarki (HAU)

35. Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Attaura, ya yi masa tambaya, yana gwada shi, ya ce,

36. “Malam, wane umarni ne mafi girma a cikin Attaura?”

37. Ya ce masa, “Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.

38. Wannan shi ne babban umarni na farko.

39. Na biyu kuma kamarsa yake, ‘Ka ƙaunaci ɗan'uwanka kamar kanka.’

40. A kan umarnin nan biyu duk Attaura da koyarwar annabawa suka rataya.”

41. Tun Farisiyawa suna tare gu ɗaya, sai Yesu ya yi musu tambaya,

Mat 22