Mat 21:37-42 Littafi Mai Tsarki (HAU)

37. Daga baya sai ya aiki ɗansa gare su, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’

38. Amma da manoman suka ga ɗan, suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magajin, ku zo mu kashe shi, gādonsa ya zama namu.’

39. Sai suka kama shi, suka jefa shi bayan shinge, suka kashe shi.

40. To, sa'ad da ubangijin garkar nan ya zo, me zai yi wa manoman nan?”

41. Sai suka ce masa, “Zai yi wa mutanen banzan nan mugun kisa, ya ba waɗansu manoma sufurinta, waɗanda za su riƙa ba shi gallar garkar a lokacin nunanta.”

42. Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karantawa a Littattafai ba? cewa,‘Dutsen da magina suka ƙi,Shi ne ya zama mafificin dutsen gini.Wannan aikin Ubangiji ne,A gare mu kuwa abin al'ajabi ne.’

Mat 21